Sojin Najeriya sun kashe 'yan bindiga da ke girbi a gonakin manoma a Zamfara
Dakarun rundunar ta musammaan ta Operation Hadarin Daji sun kashe wasu ‘yaan ta’adda a kauyen Yar Tashar da ke karamar hukumar Maru ta jihar Zamfara a arewa maso yammacin Najeriya.
Wallafawa ranar:
Rahotanni sun ce ‘yan ta’addan sun gamu da ajalinsu ne a yayin da ske kokarin girbin amfani gona daga wasu gonaki a kauyen.
Daga cikin wadanda dakarun suka kashe har da wani kasurgumin dan bindiga da aka fi sani da Bada, wanda aka ce ya kai hari kasuwar kauyen, inda ya kashe wasu manoma, kafin daga bisani ya garzaya gonakinsu don girbe hatsi.
Wani babban hafsan sojin da ke aiki a yankin, ya ce dakarunsa sun mayar da martani a kan farmakin da wasu ‘yan bindiga suka kai kaauyen Gamraki na gundumar Kwatarkwashi a karamar hukumar Bungudu ta jihar, indaa suka raba rana da ‘yan ta’addan, har suka kwato wasu mutane 2 da suka sace.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu