Isa ga babban shafi

Najerya: Hukumar tsaron DSS ta bada rahotanni 44 gabanin harin Kuje -Wase

Mataimakin shugaban majalisar wakilan Najeriya  Ahmed Idris Wase, ya bayyana cewa hukumar tsaron DSS ta gabatar da rahotanni a kan tsaro har guda 44   gabanin harin gidan yarin Kuje.

Misali na 'yan bindiga.
Misali na 'yan bindiga. © Daily Trust
Talla

A ranar 5 da watan Yuli ne ‘yan ta’adda suka kutsa gidan yarin Kuje da kje birnin Tarayyar Najeriya a Anuja, inda suka kubutr da sama da mutane 800 da ke daure a gidan, ciki har da ‘yan kungiyar Boko Haram da aka tsare.

Ya  bayyana haka ne  a yayin da yake tsokaci a kan kudirin da aka gabatar a majalisar a game da haramta amfani da Babura wajen sufuri a fadin kasar, wadda gwamnatin kasar take duba yiwuwar aiwatarwa.

Dan majalisa,  Abubakar Makki Yelleman daga jihar Jigawa ne ya gabatar da kudirin a taron majalisar a yau Talata.

Wase ya ce lallai ya ga rahotani har 44 da hukumar tsaron DSS ta mika wa gwamnati a game da tsaro gabanin harin da ‘yan ta’adda suka kai gidan yarin Kuje.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.