Ba zan huta ba sai na lalubo wa ‘yan Najeriya sauki - Buhari
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhariya tabbatar wa da ‘yan Najeriya cewa ba zai hut aba har sai ya kawo musu sauki a kan matsalolin da ke damun su da suka hada da tsaro da tsadar rayuwa.
Wallafawa ranar:
Shugaban ya bada wannan tabbacin ne a sakonsa na Sallah ga al’ummar Musulmi da sauran ‘yan kasa.
A wata sanarwa da mai taimaka masa a harkar yada labarai, Malam Garba Shehu ya raba, Buhari ya ce yana sane da halin kunci da al’ummar kasar ke ciki, kuma yana aiki tukuru don warware su.
Shugaba Buhari ya bayyana fatan cewa wannan lokaci na Sallah babba zai kasance silar samun albarka da zaman lafiya da ci gaban ‘yan Najeriya, yana mai bayyana ykinin cewa zamantakewa da kwanciyar hankali za su inganta a kasar.
Shugaban ya shawarci Musulmai da su yi riko da koyarwar addininsu don ganin daidai a al’amuransu.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu