Isa ga babban shafi
Najeriya - 'Yan bindiga

An sake sace Dalibai Mata a wani kwalajin Zamfara

An sace wasu mutane da suka hada da dalibai mata na Kwalejin koyar da harkokin kiwon Lafiya ta Zamfara dake Tsafe.

Jami'an tsaron Najeriiya a harabar makarantar sakandaren Jangebe dake jihar Zamfara.
Jami'an tsaron Najeriiya a harabar makarantar sakandaren Jangebe dake jihar Zamfara. AP - Ibrahim Mansur
Talla

Wani malamin kwalejin da ya nemi a sakaya sunansa, ya tabbatar wa Jaridar Daily Trust lamarin da safiyar Laraba.

Ya ce masu garkuwa da mutanen sun yi awon gaba da daliban ne a dakin kwanansu da ke wajen harabar makarantar.

Ba a dai san adadin daliban da aka yi garkuwa da su ba, amma wata majiya ta shaida wa Daily Trust cewa ‘yan bindigar sun yi awon gaba da dalibai biyar.

Lamarin ya zo ne mako guda bayan da aka harbe dan Mamman Tsafe, kwamishinan gwamnatin Gwamna Bello Matawalle a kofar gidan mahaifinsa da ke Tsafe.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.