Isa ga babban shafi

An dakatar da limamin Masallacin Juma'a na Apo saboda sukar gwamnati

Kwamitin kula da babban masallacin Juma’a na Apo Kwatas dake birnin Abuja a Najeriya, ya dakatar da limamin Masallacin Shiekh Nura Khalid sakamakon kalaman da ya furta yayin gabatar da hudubar Sallar Juma'ar da ta gabata.

Sheikh Muhammad Nura Khalid, limamin masallacin Juma'a na Apo dake birnin Abuja da aka dakatar saboda sukar gwamnati akan matsalar tsaro.
Sheikh Muhammad Nura Khalid, limamin masallacin Juma'a na Apo dake birnin Abuja da aka dakatar saboda sukar gwamnati akan matsalar tsaro. © Wikipedia
Talla

Yayin jawabin da ya gabatar, malamin ya bukaci jama’a da kada su fita zabe har sai cimma yarjejeniya tsakanin mutane da ‘yan siyasa kan kare hakkokinsu.

Malamin ya kuma caccaki gwamnati kan gazawar ta wajen magance matsalolin tsaron da suka addabi ‘yan Najeriya.

Sai dai a cikin wata sanarwa shugaban kwamitin kula da Masallacin na APO, kuma tsohon Sanata Sa’idu Muhammad Dansadau ya ce kamata yayi malamin ya shawarci mutane da su ki zabar baragurbin ‘yan siyasa zuwa kan mukamai, amma ba ya furta kalaman tunzura su kin fita zaben ba.

Shiekh Nura Khalid dai yayi fice wajen jan hankalin hukumomi a Najeriya a duk lokacin da yake ganin an aikata ba daidai ba, inda a lokuta da dama ya ke amfani da kakkausan harshe wajen sukar da ya kan yi.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.