'Yan bindiga sun sace mutane 11 a wani kauyen Katsina bayan janye sojoji
A Najeriya, biyo bayan janyewar da sojoji suka yi a kauyen Shimfida na karamar hukumar Jibia a jihar Katsina, ‘yan bindiga sun shiga kauyen a daren Juma’a, inda suka yi awon gaba da mutane 11.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Tun da farko sashen Hausa na RFI ya kawo rahoton yadda mutane 7 suka mutu a sakamakon wani turmitsitsi da ya auku a lokacin da dimbim jama’a ke barin kauyen sakamakon janye sojoji da hukumomin kasar suka yi.
A makarantar sakanadiren gwamnati ta Shimfida, mai nisan kilomita 27 daga garin Jibia ne da ma aka girke sojojin da aka janye a ranar Alhamis da ta gabata.
Shimfida na daya daga cikin yankunan da ayyukan ‘yan bindiga, masu satar mutane da yi wa mata fyade suka yi wa mummunar illa a jihar Katsina da ke arewa maso yammacin Najeriya.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu