Isa ga babban shafi
Najeriya - Hakkin dan Adam

Kotun ECOWAS ta bukaci Najeriya ta biya wani dan jarida diyyar miliyan 30

Kotun ECOWAS da ke zamanta a Abuja babban birnin tarayyar Najeriya ta bukaci gwamnatin Tarayya da jihar Cross River da su biya dan jarida Agba Jalingo Naira miliyan 30 a matsayin diyya, sakamkon tsare shi ba bisa ka’ida ba, da kuma azabtar da shi.

Alamar shari'a a Najeriya
Alamar shari'a a Najeriya The Guardian
Talla

A wani hukunci da mambobin alkalai uku suka gabatar ranar Jumma'a  karkashin jagorancin shugaban kotun, mai shara’a Edward Amoako Asante, sun ce gwamnatin Najeriya ta sabawa tanade-tanaden ka'idojin adalci na duniya, musamman, Yarjejeniyar Afirka kan kare hakkin Dan Adam, wanda Nijeriya ta sanya hanu.

A cewar kotun, “An kama Agba Jalingo kuma an daure shi da mari har na tsawon kwanaki 34 ba tare da gurfanar da shi a gaban kotu ba. Abin da ke tabbatar da take hakkokinsa da cin zarafinsa.

Kungiyar SERAP ta shigar da kara a madadin dan jaridar, biyo bayan kamun da aka yi wa Jalingo a ranar 22 ga watan Agustan shekarar 2019 bayan da ya wallafa wani labari a jaridar sa ta yanar gizo, ‘Cross River Watch,’ da ke cewa Gwamna Ben Ayade ya karkatar da N500m na ​​jihar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.