Isa ga babban shafi
Najeriya-Katsina

'Yan sandan Katsina sun kashe dan bindiga tare da ceto wani mutum da dabbobi

‘Yan sanda sun yi nasarar kashe wani dan bindiga, kana suka ceto wani wanda aka sace bayan wata musayar wuta da ‘yan bindigar da suka kutsa kauyen Kwanar Kodo dake karamar hukumar Kankara ta jihar Katsina a Najeriya.

Jami'an 'yansandan Najeriya.
Jami'an 'yansandan Najeriya. REUTERS/Afolabi Sotunde
Talla

‘Yan sandan sun kuma kwato shanu 20 da rahuna 100 a wani samame da suka kai kusan karshen mako.

Rahotanni sun ce ‘yan bindigar sun shiga kauyen Kwanar Kodon ne da misalin karfe 2:30 na daren  Juma’a sukaa kuma dauki wani mutum mai suna Alhaji Sanusi Adamu.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar SP Gambi Isa ya tabbatar da aukuwar lamarin.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.