'Yan bindiga sun bukaci biyan kudin fansar marayun da suka sace a Abuja
‘Yan bindigar da suka sace wasu marayu daga gidan da ake kula da su a birnin Abuja dake Najeriya sun bukaci a biyan diyyar naira miliyan 10 akan kowanne maraya guda kafin sakinsa.
Wallafawa ranar:
‘Yan bindigar sun kuma bukaci biyan naira miliyan goma kan mai gadin gidan da wani magidanci Momoh Jimoh da iyalinsa, da kuma wata mata Rukaiyat Salihu.
Wata majiya a gidan marayun ta shaidawa Jaridar Daily Trust cewar, ‘yan bindigar sun buga waya a ranakun Lahadi da jiya Litinin domin neman diyyar.
Wani dan uwan magidancin da aka sace ya tabbatar da bukatar biyan diyyar, sai dai rundunar ‘yan sandan Abuja bata ce komai ba dangane da bukatar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu