'Yan bindiga sun kaiwa tawagar Sarkin Kauran Namoda farmaki
‘Yan bindiga sun kaiwa tawagar motocin Sarkin Kaura Namoda Alhaji Sunusi Muhammad dake jihar Zamfara farmaki, inda suka halaka akalla mutane 8, tare da jikkata wasu da dama.
Wallafawa ranar:
Wani da ya tsira daga farmakin ya ce ‘yan bindigar sun yiwa tawagar Sarkin kwanton Bauna ne akan hanyar Zaria zuwa Funtua, lokacin da suke kokarin komawa garin Gusau daga Abuja.
Bayanai sun ce cikin wadanda suka rasa rayukansu a farmakin akwai direba guda da kuma ‘yan sanda uku, sai dai Sarkin na Kaura Namoda ya tsira ba tare da samun rauni ba.
Rundunar ‘yan sandan Najeriya dake Katsina ta tabbatar da aukuwar lamarin sai dai ba ta yi karin bayani akai ba.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu