'Yan bindiga sun halaka sojoji 16 a Katsina
Gungun 'yan bindiga sun halaka sojojin Najeriya 16 a jihar Katsina, tare da jikkata wasu kalla 28, bayanda suka yi musu kwanton bauna.
Wallafawa ranar:
Majiyoyin tsaro, sun ce maharan sun farwa dakarun sojin daga saman duwatsu ne a lokacin da suke tattakin sintiri a karamar hukumar Jibiya da misalin karfe 6 na yammacin jiya asabar.
Sai dai har yanzu rundunar sojin ba ta ce komai ba kan farmakin.
Katsina na daga cikin jihohin arewacin Najeriya masu fama da matsalar hare-haren ‘yan bindiga dake halaka rayukan jama’a, da kuma satar mutanen don karbar kudin fansa.
Wani rahoton cibiyar sa ido kan samar da zaman lafiya a Afrika ta Yamma, yace hare-haren ‘yan bindiga a jihar Katsina yayin sanadin mutuwar sama da mutane dubu 2, tarwatsa kauyuka 500, da kuma raba sama da mutane dubu 33 da muhallansu.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu