Ba za mu bude Masallatai da Coci ba-gwamnatin Lagos
Gwamnatin jihar Lagos da ke kudancin Najeriya ta ce, ba za ta gaggauta bude Masallatai da Coci-coci ba ga masu ibada a jihar.
Wallafawa ranar:
Kwamishinan Cikin Gida, Prince Anofiu Elegushi ya bayyana haka a gefen taron bitar cika shekara guda da gwamnann jihar Babajide Sanwo-Olu ya yi a kan karaga.
Elegushi ya ce, har yanzu Lagos ce cibiyar annobar coronavirus, a don haka babu yadda za a bude wuraren ibada cikin hanzari.
Tun a ranar Litinin gwamnatin tarayya ta janye dokar hana taruwar ibada a Masallatai da Majami’u a fadin Najeriya, amma ta ce, aiwatar da matakin ya ta’allaka da sharuddan da gwamnoni jihohi suka amince da su.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu