Isa ga babban shafi
Najeriya

Ba za mu bude Masallatai da Coci ba-gwamnatin Lagos

Gwamnatin jihar Lagos da ke kudancin Najeriya ta ce, ba za ta gaggauta bude Masallatai da Coci-coci ba ga masu ibada a jihar.

Gwamnan Jihar Legas Babajide Sanwo-Olu, tare da mataimakinsa Obafemi Hamzat daga hadu, sai kuma kwamishinansa na lafiya Farfesa Akin Abayomi.
Gwamnan Jihar Legas Babajide Sanwo-Olu, tare da mataimakinsa Obafemi Hamzat daga hadu, sai kuma kwamishinansa na lafiya Farfesa Akin Abayomi. LASG
Talla

Kwamishinan Cikin Gida, Prince Anofiu Elegushi ya bayyana haka a gefen taron bitar cika shekara guda da gwamnann jihar Babajide Sanwo-Olu ya yi a kan karaga.

Elegushi ya ce, har yanzu Lagos ce cibiyar annobar coronavirus, a don haka babu yadda za a bude wuraren ibada cikin hanzari.

Tun a ranar Litinin gwamnatin tarayya ta janye dokar hana taruwar ibada a Masallatai da Majami’u a fadin Najeriya, amma ta ce, aiwatar da matakin ya ta’allaka da sharuddan da gwamnoni jihohi suka amince da su.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.