Isa ga babban shafi
Najeriya

Jiga-jigan PDP sun yi zanga-zanga a Abuja

Shugabannin Jam’iyyar PDP mai adawa a Najeriya sun gudanar da zanga-zanga a birnin Abuja don nuna rashin amincewarsu da sakamakon zaben gwamnan jihar Osun.

Wasu daga cikin jiga-jigan PDP da suka halarci zanga-zangar a Abuja
Wasu daga cikin jiga-jigan PDP da suka halarci zanga-zangar a Abuja Punchnewspaper
Talla

Shugabannin da suka hada da Bukola Saraki, Kakakin Majalisar Dattawan kasar da Yakubu Dogara, Kakakin Majalisar Wakilai da Uche Secondus, shugaban Jam’iyyar PDP na kasa, su ne suka jagoranci zanga-zangar a shalkwatan Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta, INEC.

Sauran mahalarta zanga-zangar sun hada da Gwamnan jihar Sokoto, Aminu Tambuwal da tsohon Gwamnan Jigawa, Sule Lamido da kuma Sanata Dino Melaye.

Masu zanga-zangar na bukatar INEC ta ayyana dan takarar PDP , Ademola Adeleke a matsayin wanda ta lashe zaben na jihar Osun.

Tuni dai INEC ta ayyana  Ogboyega Oyetola na APC a matsayin wanda ya yi nasara a zaben na makon jiya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.