Gwamnatin Legas zata rushe babbar mayankar jihar
Gwamnatin Lagos a Najeriya ta umurci masu sayar da dabbobi a babbar mayakan jihar wato abbatoir da ke Agege, da su tattara nasu ya nasu su bar wurin, domin za a rusa wurin nan ba da jimawa ba.
Wallafawa ranar:
Hakan yasa shugabancin ‘yan kasuwar dabbobin suka bukaci masu fataucin shanu daga arewa zuwa Lagos da su dakatar da wannan fatauci har sai abin da halin ya yi.
Har yanzu dai gwamnatin jihar ta Lagos bata kayyade wa’adin da ta debawa masu gudanar da sana’arsu a mayankar ba.
Wannan matakin ne yasa yayin zantawarsa da sashin hausa na RFI, Alhaji Abdullahi Liliga, shugaban Miyatti a jihar ta Lagos, ya bayyana cewa matakin tamkar bita da kulli gwamnati ke nufinsu da shi, kasancewar hatta wurin wucin gadin da ta basu a yanzu kuma ta ce shima rusa shi zata yi.
Gwamnatin Legas zata rushe babbar mayankar jihar
Bincike ya nuna cewa akalla shanu da sauran dabbobi, 8,000 ne ake yankawa kowace rana Lagos, wadanda aka kiyasta kudinsu zai kai Naira biliyan daya da rabi.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu