Isa ga babban shafi
Najeriya

Fadar gwamnati ta musunta rade-rade kan takarar Buhari

Fadar gwamnatin Najeriya ta musanta rahotanni da ke cewa shugaba Muhammadu Buhari ba shi da tabbacin sake tsayawa takara a zaben shugabancin kasar da za a gudanar a shekarar 2019.

Shugaban kasar Najeriya Mohammadu Buhari
Shugaban kasar Najeriya Mohammadu Buhari Sunday AGHAEZE / NIGERIA STATE HOUSE / AFP
Talla

Sanarwar na zuwa ne yayin da ake ci gaba da rade-radin yiwuwar sake takarar shugaban a zaben shekara mai zuwa.

A baya-bayanan ministan sadarwa kasar Adebayo Shittu wanda ya bada gudunmawa wajen nasaran zaben Buhari a zaben 2015 ya ce, zai jagoranci kungiyar magoya bayan Buhari don yi ma sa yakin neman zabe.

Ana saran gudanar da zaben shugaban kasa a ranar 16 ga watan Fabairun 2019, yayin da jam'iyyun siyasa za su gabatar da ‘yan takaransu daga ranar 18 ga watan agusta zuwa 7 ga watan Oktoba.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.