Isa ga babban shafi
Wasanni

Super Eagles zasu dafe dala 20,000 kan kowace kwallo a ragar Kamaru

Wani shahararren dan Kasuwa a Najeriya yayiwa tawagar kwallon kafa ta kasar Super Eagles alkawarin cewa zai basu kyautar dala Dubu 20,000, kwatankwacin naira miliyan da dubu dari da saba’in (7,170,000) kan kowace kwallo da su jefa a ragar Kamaru a wasan da zasu fafata yau na neman cancantar zuwa gasar cin kofin duniya ta badi, a birnin Yaounde.

Tawagar 'yan wasan Najeriya yayinda suke murnar lallasa Kamaru da kwallaye 4-0 a wasan neman cancantar zuwa gasar cin kofin duniya na shekarar 2018 da za'a yi a Rasha.
Tawagar 'yan wasan Najeriya yayinda suke murnar lallasa Kamaru da kwallaye 4-0 a wasan neman cancantar zuwa gasar cin kofin duniya na shekarar 2018 da za'a yi a Rasha. Nairaland
Talla

Attajirin da ke amsa sunan Udofia, ya sha alwashin yi wa ‘yan wasan na super eagles yayyafin kudin ne sakamakon farin cikin yadda suka lallasa Kamaru da kwallaye 4 – 0 a zagayen farko da suka fafata a garin Uyo.

A halin da ake ciki a yadda jadawalin tsayuwar rukunan kasashen da ke fafata neman cancantar zuwar gasar cin kofin duniyar da za’a yi a Rasha, Najeriya ce kan gaba a rukunin da take ciki na B da maki 9, sai Zambia da maki 4, Kamaru ce ta uku da maki 2 yayinda Algeria ke matsayi na karshe da maki 1.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.