Isa ga babban shafi
Najeriya

Wasu mayaka sun kai hari a Adamawa

Wasu mutane da ake zargin ‘yan Boko Haram ne sun kai hare-hare a cikin daren da ya gabata a wasu yankuna na jihar Adamawa da ke arewa maso gabashin Najeriya.

Mayakan da ake zargin na Boko Haram ne sun kona gidaje da masallatai a harin da suka kai a karamar hukumar Madagali ta Adamawa a Najeriya
Mayakan da ake zargin na Boko Haram ne sun kona gidaje da masallatai a harin da suka kai a karamar hukumar Madagali ta Adamawa a Najeriya AFP PHOTO / STRINGER
Talla

Mutanen yankunan sun kauracewa gidajensu bayan farmakin da mayakan suka kaddamar a Nyibango da Muduhu da ke karamar hukumar Madagali.

Farmakin na zuwa ne kwanakin kalilan da aka kai makamancinsa a kauyen Mildu da ke makwabtaka da yankunan, in da mutane bakwai suka rasa rayukansu.

A yayin zantawa da manema labarai, shugaban karamar hukumar Madagali, Yusuf Muhammad ya ce, mayakan sun dauki tsawon sa’oi biyu suna kai hare-haren.

Mayakan sun kona gidaje da dama tare da sace kayayyakin abincin jama’a kamar yadda shugaban karamar hukumar ya tabbatar.

A cewarsa, kawo yanzu, ba a tantance adadin mutanen da suka mutu ba da kuma wadanda suka samu rauni.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.