Najeriya
Babbar Kotun Lagos Ta Mallakawa Gwamnati Kudaden da aka tsinta Kusan Naira Miliyan 500
Babbar Kotun Lagos ta bada umarni na karshe na kwace wasu kudaden kasar Naira kusan miliyan 450 da aka samu a wani shago na ‘yan chanji dake Lagos, kasancewar har yanzu babu wanda ya zo karban kudaden.
Wallafawa ranar:
Talla
Mai sharia Rilwan Aikawa ya bada wannan umarni bayan ya saurari bayanai daga masu shigar da kara wato Hukumar EFCC.
A cewar Alkalin tunda babu mai su, kudaden sun zama mallakin Gwamnatin Tarayyar Najeriya.
Wata daya kenan da gano wadannan makudan kudade cikin buhuhuna amma har yanzu babu wanda ya amsa cewa nashi ne duk da cigiya da aka yi ta yi.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu