Isa ga babban shafi
Nigeria

Matsalar Karancin Man Fetur Yayi Kamari a Nigeria

Rahotanni daga sassan Nigeria na cewa ana ci gaba da fuskantar matsanancin karancin man fetur, inda ake samun dogayen layukan ababan hawa a gidajen sai da mai, yayin da  wasu masu ababan hawa suka maida motocin su wuraren da suke kwana a harabar gidajen sai da man fetur.  

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari rfi
Talla

Manyan biranen kasar musamman Lagos, Ibadan, Enugu da Yanagoa, da sauran garuruwan dake arewacin kasar, bayanai na nuna lamarin ya yi kamari sosai.

Farashin da ake sayarwa a kasuwannin bayan fage kan nunka kayyadadden farashin har sau hudu.

Gwamnatin kasar taki fitowa da bayanai  na takamaiman dalilan da suka haddasa wannan matsala.

Wasu masu lura da lamurran kasar kan rika dora laifin kan rashin zama cikin kasa da Shugaba Muhammadu Buhari baya yi domin ya tunkari matsalolin sosai duk da cewa shine Ministan Harkokin Man Fetur.

 

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.