'Yan Maiduguri na kukan rashin kudi a Najeriya
Mutanen birnin Maiduguri na jihar Bornon na Najeriya na kukan rashin kudi a hannayensu duk da samun walwala da dawowar rayuwa a Jiharsu mai fama da rikicin Boko Haram. Kodayake, kungiyoyin sa-kai na ciki da waje da ke shiga Maiduguri na taimakawa wajen samun yawaitar kudade ga jama'a da kuma 'yan kasuwa. Amma wasu na ganin rashin hada-hadar kasuwanci a manyan hanyoyin da suka hada Najeriya da Kamaru da Nijar da Chadi ne suka haifar da matsalar karancin kudin a hannayen jama'a a jihar Borno. Awwal Janyau da ya kai ziyara ta musamman a Maiduguri ya hada mana rahoto.
Wallafawa ranar:
'Yan Maiduguri na kukan rashim kudi
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu