Isa ga babban shafi
Najeriya

Najeriya ta kafa hukumar sa ido kan farashin kayan masarufi

Majalisar zartawar Najeriya ta cimma matsayar kafa wata hukuma ta musamman, da zata sa ido da zata magance hauhawar farashin kayayyakin masarufi a kasar.

Mataimakin Shugaban Najeriya Farfesa Yemi Osinbajo
Mataimakin Shugaban Najeriya Farfesa Yemi Osinbajo
Talla

Minsitan yada labaran kasar Lai Mohammed ya sanar da matakin, yayin zantawar da yayi da manema labarai a garin Abuja, jim kadan bayan kamalla taron majalisar, wanda mukaddashin shugaban Najeriya Farfesa Yemi Osinbajo ya jagoranta.

Lai Mohammed ya ce ana fatan kafa kwamitin zai kawo karshen yawaitar hauhawar farashin kayan abinci a Najeriya, wanda hakan ya jefa masu kananan karfi cikin mawuyacin hali a kasar.

Daga cikin wadanda zasu jagoranci hukumar sa idon kan farashin kayan abincin, akwai Ministoci da suka hadar da na sassan albarkatun gona, ma’aikatar kudi, Sufuri, da kuma na albarkatun ruwa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.