Sojan Nigeria Sun Sake Bude Hanyar Damaturu zuwa Biu
Hafsan sojan Nigeria Laftanar Janar Tukur Buratai, ya sake bude hanyar Damaturu zuwa Biu mai nisan kilomita 132 wanda aka dauki lokaci mai tsawo hanyar na rufe saboda matsalar ‘yan kungiyar Boko Haram
Wallafawa ranar:
Laftanar Janar Tukur Buratai da kansa ya jagoranci sake kaddamar da hanyar, a wani buki da akayi a Buniyadi, inda yayi fatan hakan zai farfado da harkokin tattalin arziki da ciniki a yankin arewa maso gabashin kasar.
A jawabin sa Gwamnan Jihar Yobe Ibrahim Geidam ya yaba da sake bude hanyar domin ganin harkokin zirga-zirga da tattalin arzikin yankin sun inganta.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu