Kotun Najeriya ta daure mutane 7 saboda harkar man fetir
Hukumar da ke ya ki da masu yi wa tattalin arzikin Najeriya zagon kasa, wato EFCC ta bayyana cewa Kotu ta yanke wa wasu mutane 7 hukuncin daurin shekaru 10 a gidan yari bayan an kama su da kusan tan dubu 1 da 500 na Man fetur da suka shigo da su cikin kasar ta barauniyar hanya.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Wannan dai na zuwa ne bayan gwamnatin kasar ta kudiri aniyar sa kafar wando daya da masu harkar man fetur ba bisa ka’ida ba a kasar.
Dukkanin mutanen bakwai ‘yan asalin Najeriya ne, kuma a jiya jumma’a ne babban kotun tarayya da ke jihar Lagos ta same su da aiakata laifin.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu