'Yar kunar bakin wake ta kai harin bam a kano
'Yan sanda Jihar kano da ke Najeriya sun tabbatar da cewa wata yarinya da ta kai harin kunar bakin wake a kusa da Masallaci Aliyu bin abu Talib da ke kusa da shataletalen 'Dangi' ita kadai ta rasa ranta, sai mutum guda da ya jikata.
Wallafawa ranar:
Harin dai ya afku ne da misalin karfe 9 da 'yan mintina agoggon Najeriya, bayan kammala sallah Taraweeh a masallacin.
Wakilin RFI a kano Abubakar Isa Dandago ya rawaito cewa wani ganau ya shaida masa cewa yaga wata yarinya a lokacin da ta ke barin masallacin, kuma ya ga sassan jikinta a kasa bayan fashewar bam din.
Abubakar Isa Dandago dauke da Rahoto kan Harin kunar bakin wake a Masallacin Aliyu Bin Abi talib
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu