Najeriya
Dubban mutanen Kano sun tarbi Hamza al Mustapha
Dubban mutanen Kano ne suka yi tururuwa don tarbar Manjo Hamza al Mustapha tsohon Dogarin Marigayi Janar Sani Abacha, da kotun Daukaka kara ta wanke daga hukuncin kisan da wata kotu ta yanke masa. A cikin Rahoton Abubakar Isa Dandago zaku ji ‘Yar al Mustapha mai suna Fatima tana bayyana farin cikinta saboda tun tana jaririya aka daure Mahaifinta wanda ya kwashe tsawon shekaru kusan 15 a rufe.
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:29