Heartland da Lobi Stars za su nemi lashe kofin Kalubale a Najeriya
Kungiyar Heartland da Lobi Stars a Najeriya sune za su buga wasan karshe na neman lashe kofin kalubale da za’a buga a ranar Lahadi a birnin Lagos, bayan sun samu nasarar lashe wasan kusa da karshe.
Wallafawa ranar:
A jiya Laraba ne Heartland ta doke Prime FC a bugun daga kai sai mai tsaron gida, bayan kammala wasan babu ci a birnin Ilori.
A daya bangaren ma, Lobi Stars ta samu nasarar doke Kano Pillers a bugun daga kai sai mai tsaron gida bayan kammala lokuttan wasan babu kwallo a raga.
Lobi Stars dai ta taba lashe kofin a shekarar 2003 bayan doke kungiyar Sharks ci 2-0. Sannan kungiyar ta taba buga wasan karshe tsakaninta da Eyimba a shekarar 2005 amma Eyimba ce ta lashe kofin.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu