Yan Bindiga sun yi yunkuri fasa gidan fursuna a Najeriya
Rohotanni daga garin Gombe fadar gwamnatin Jihar Gombe da ke Tarayyar Najeriya sun tabbatar da mutuwan mutane 12, yayin da ‘yan bindiga suka yi yunkurin fasa gidan fursuna.
Wallafawa ranar:
Kwamishinan ‘yan sandan Jihar Gandi Ebikeme Orubebe ya shaida wa manema labarai cewa jami’an tsaro sun mayar da martani tare da cin karfi maharan bayan kwashe sa’oi biyu ana musanyen wuta tare da amfani da bababe masu fashewa daga tsagerun.
Akwai ‘yan sanda biyu da suke cikin wadanda suka rasa ransu, soja daya ya samu raunika, sauran mutane 10 akasari maharan suka hallaka.
A wani labarin, wasu maharan sun hallaka mutane biyar a Masallaci da ke garin Kano birni mafi girma da ke yankin Arewacin Tarayyar ta Najeriya.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu