Thailand
Masu Zanga Zanga sun kawar da Yuwuwar Tattaunawa da gwamnati
Masu zanga zangar kasar Thailand da ke sanye da jajanyen kaya, sun kawar da yuwuwar ganawa da gwamnatin kasar. Farkon wannan watan aka yi dauki ba dadi tsakanin masu zanga zangar magoya bayan hambararren Prime Minista Thaksin Shinawatra.Daya daga cikin shugabannin masu zanga zangar ya bayyana cewa arangamar da aka yi ranar 10 ga wannan wata, ta kawar da duk wata fatar zaman teburi guda da gwamnatin kasar, domin sasantawa.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar: