Isa ga babban shafi

Kimanin Falasdinawa dubu 3 suka mutu sanadiyar hare-haren Isra'ila

Sabbin alkaluman hukumomi sun nuna cewa, ya zuwa yanzu, an kashe Falasdinawa dubu 2 da 808, yayin da Isra’ila ta samu asarar rayukan mutane dubu 1 da 400 sakamakon yakin da ake gwabzawa a Gaza. 

Yadda wasu Falasdinawa ke kukan kashe 'yan uwansu da Isra'ila ta yi.
Yadda wasu Falasdinawa ke kukan kashe 'yan uwansu da Isra'ila ta yi. AP - Fatima Shbair
Talla

 

Alkaluman sun kuma nuna cewa, an samu mutane dubu 3 da 500 da suka jikkata a bangaren Isra’ila, yayin da Falasdinawa dubu 10 da 859 su ma suka samu rauni a yakin na Gaza. 

A can yankin Yamma ga Kogin Jordan kuwa, an samu asarar rayukan mutane akalla 57, inda kuma sama da dubu 1 da 200 suka jikkata. 

 

Alkaluman da kafafen yada labarai da ofishin gwamnati suka tattara a Gaza, sun nuna cewa, kashi 64 cikin 100 na mamatan da harin ya rutsa da su mata ne da kananan yara. 

Mayakan Hamas sun bayyana cewa, sun kaddamar sabbin hare-haren makaman roka a yankin  birnin Kudus da kuma Tel Aviv a matsayin martani kan farkamakin da suka ce sojojin Isra’ila ke kai wa fararen hula. 

Dubun dubatar 'yan kasar Jordan a birnin Amman, yayin zanga-zangar goyon baya ga Falasdinawa a Gaza.
Dubun dubatar 'yan kasar Jordan a birnin Amman, yayin zanga-zangar goyon baya ga Falasdinawa a Gaza. REUTERS - ALAA AL SUKHNI

Yanzu haka Falasdinawa sun gudanar da wata zanga-zanga a cikin unguwanni a sassan Yankin Yamma ga Kogin Jordan, suna kira da a kawo karshen hare-haren Isra’ila a zirin Gaza. 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.