Isa ga babban shafi

Biden ya ce Amurka za ta ci gaba da bibiyar lammuran Gabas ta Tsakiya

Shugaban Amurka Joe Biden ya bar kasar Saudiyya a cikin jirginsa na Air Fiorce One a yau Asabar, lamarin da ke kawo karshen ziyararsa ta farko a yankin tun da ya hau karagar mulki, inda ya shafe kwanaki 4.

Shugaban Amurka Joe Biden a Birnin Kudus, ranar 14/07/2022.
Shugaban Amurka Joe Biden a Birnin Kudus, ranar 14/07/2022. AP - Ronen Zvulun
Talla

Kafofin yada labaran Saudiyya sun ruwaito cewa gwamnan lardin Makka, yerima Khaled-Faisal ne ya yi wa shugaba Biden rakiya zuwa filin tashi da saukar jiragen sama na Jidda.

Tun da farko a Asabar din nan, shugaba  Biden  ya shaida wa shugabannin kasashen Larabawa cewa Amurka ba za ta ci gaba da bibiyar lammuran yankin Gabas ta Tsakiya, kuma ba za ta bari wata kasa cikin manyan kasashen duniya ta yi mata zarra a yankin ba.

Biden ya yi wannan bayanin ne a wani taron da ya yi da shugabannin kasashe 6 da ke cikin kungiyar hadin kan kasashen yankin tekun Fasha.

A ranar Juma’a, biden ya tattauna da yerima mai jiran  gado na kasar Saudiyya, Mohamed bin Salman, kuma a nan ne ya tabo batun kisan dan jaridan nan, Jamal Khashoggi, inda yai yi gargadin cewa a daina musguna wa masu mabanbantan ra’ayi.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.