Isa ga babban shafi

Biden na ziyara a yankin Gabas ta Tsakiya

Shugaban Amurka Joe Biden ya fara ziyarar a yankin Gabas ta Tsakiya daga kasar Isra’ila, inda a ganawarsa ta farko da shugabannin kasar, suka sha alwashin hada karfi domin fuskantar babbar abokiyar hamayyarsu Iran.

Shugaban Amurka Joe Biden yayin gaisawa da takwarorinsa na Isra'ila, bayan sauka a filin jiragen sama na birnin Tel Aviv.
Shugaban Amurka Joe Biden yayin gaisawa da takwarorinsa na Isra'ila, bayan sauka a filin jiragen sama na birnin Tel Aviv. AP - Evan Vucci
Talla

Tuni dai ta bayyana cewa, tattaunawar Biden da shugabannin Isra’ila za ta fi mayar da hankali ne kan Iran, kamar yadda mai rikon kwaryar mukamin Fira Minista kasar ta Isra’ila Yair Lapid ya tabbatar, a lokacin da ya tarbi shugaban Amurka a filin jirgin sama.

A ranar Juma’a ne kuma ake sa ran Biden zai yi tattaki zuwa Saudiya, inda ake sa ran sai gana da shugabannin kasar kan kokarin kulla kyakkyawar alaka tsakaninsu da Isra’ila, kasar da har yanzu masarautar ba ta amince da wanzuwarta ba.

Masu sharhi dai na ganin ko shakkah babu, ziyarar da Biden ke yi a Isra’ila za ta sake fusata shugabannin Falasdinawa, wadanda suke tuhumar Amurka da gazawa wajen dakatar da cin zalin da Yahudawa ke yi musu.

Shi kuwa shugaban Iran Ibrahim Raisi gargardin shugaban Amurka yayi kan cewar babu yadda za a yi ya cimma burin karfafa tsaron Isra’ila domin tabbatar da fifikonta a gabas ta tsakiya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.