Wani gwamna a Yemen ya tsallake rijiya da baya bayan harin da ya kashe mutane 5
Akalla mutane biyar suka mutu a kasar Yemen, sakamakon wani harin bam da aka kai da mota da nufin hallaka gwamnan lardin Aden, na gwamnatin da kasashen duniya suka amince da shi, kamar yadda majiyoyin tsaro a suka tabbatar a wannan Lahadi.
Wallafawa ranar:
Aden, dake kudancin Yaman, tinga ce ga masu fafutukar neman ballewa, wanda a bara ta shiga hannun gwamnatin, kuma yanki ne da ya dade ana goyawa 'yan tawayen Huthi baya a yakin da aka dade ana fafatawa.
A yayin wannan hari dai, Gwamnan Aden Ahmed Lamlas da Salem al-Socotri, wani minista na gwamnati, duk sun tsallake rijiya da baya a cewar majaiyoyin.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu