Isa ga babban shafi
Lebanon-Hariri

Ba zan iya jagorancin Lebanon ba-Hariri

Firaministan Labanon Saad Hariri da aka zaba domin kafa sabuwar sabuwar gwamnati ya yi watsi da kwallon mangwaro domin ya huta da kuda, yana mai cewa,  ba zai iya jagoranci ba a daidai wannan lokaci da kasar ke cikin gagarumar matsalar tattalin ariziki mafi muni a tarihita.

Firaministan Lebanon Sa'ad Hairi
Firaministan Lebanon Sa'ad Hairi ANWAR AMRO AFP/File
Talla

A watan Octoban 2020 ne aka zabi Hariri a matsayin Firaministan da zai kafa gwamnatin da aikinta shi ne sake fasalta hanyoyin samar da tattalin arizikin kasar da zai kai ga kasar ta cimma tallafin farfado da tattalin arizikin na kasshen duniya.

Hariri ya sanar da 'yan jarida cewa ya gana da shugaban kasar  Michel Aoun da ya bukaci ya sake fasalta shawarar jerin sunayen ministocin da za su shiga sabuwar gwamnatin da ya gabatar, wanda a kansa shi kuma ya nuna turjiya.

Da yake tsokaci kan janyewar da ke zuwa 'yan kwanaki kafin  zagayowar ranar faruwar mummunan hadarin tashar jiragen ruwan Beirut, Ministan Harakokin  Wajen Faransa Yves Le Drian ya danganta lamarin da ya faru a matsayin kullallen makirci dai ya buda sabon babi a fagen siyasar kasar sai dai ya ce  har yanzu akwai sauran lokacin yin gyara.

Wannan lamari in ji shi zai sa tarihi ya waiwayi shuwagabanin siyasar kasar ta Labanon nan gaba domin amsa kuskuren da suka aikata

Ita ma da kanta Majalisar Dinkin Duniya ta bayyana bakin cikinta kan matakin da Haririn ya dauka.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.