Dan damben Boxin din Kamaru Francis Ngannou zai kara da dan Britannia Anthony Joshua.
Dan wasan damben Boxin din nan dan kasar Kamaru Francis Ngannou, da tun a makon da ya gabata ake yada jitajitar cewa za a yi karawar da shi, zargin da ya kasance gaskiya, ida yanzu aka bayyana cewa, zai kara ne da zakaran ajin masu nauyi dan kasar Britannia Anthony Joshua.
Wallafawa ranar:
Madambacin dan kasar kamaru, Francis Ngannou zai buga wasansa na biyu a fagen damben kwararu ne a wannan shekara ta 2024.
Dan dambe dake kan ganiyar farfadowa a fagen salon damben Boxin na Mixed martial arts (MMA) da ake hada salon damben Boxin, da ke kunshe da duka da hannu, shurin kafa kokowa da kuma murkushe kato da karfin tuwa a tsakar fili, zai fuskanci wani sabon kalubale, inda zai kara da dan damben ajin masu nauyin nan dan Britannia a kasar Saudiya. Karawar da ake gani za ta dau hankali sosai.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu