Isa ga babban shafi

Ba mu shirya shiga kungiyar BRICS ba tukuna - Morocco

Kasar Morocco ta ce har yanzu ba ta gabatar da bukatar shiga kungiyar kasashen BRICS ba, kuma ba za ta halarci taron da za ta gudanar a Afirka ta Kudu ba.

Sarkin Morocco Muhammad na shida kenan yayin gabatar da jawabi ta yanar gizo ga majalisar dokokin kasar rana 8 ga watan Oktoba, 2021.
Sarkin Morocco Muhammad na shida kenan yayin gabatar da jawabi ta yanar gizo ga majalisar dokokin kasar rana 8 ga watan Oktoba, 2021. AFP - -
Talla

Da yake ambato wata majiyar diflomasiyya da ba a bayyana sunanta ba, kamfanin dillancin labaran kasar na MAP ya musanta sanarwar da ministan harkokin wajen Afirka ta Kudu Anil Sooklal ya yi, wanda ya ce a farkon wannan watan kasar Morocco na cikin kasashen da ke neman shiga kungiyar.

Kungiyar kasashe masu tasowa a halin yanzu sun hada da Brazil, Rasha, Indiya, China da Afirka ta Kudu, amma za a tattauna yiwuwar fadada ta a taron kuma Afirka ta Kudu, inda ta ce fiye da kasashe 40 ne suka nuna sha'awar shiga.

Taimakon diflomasiyya da Afirka ta Kudu ke baiwa bangaren Polisario da Aljeriya ke marawa baya, da ke neman kafa kasa mai cin gashin kanta a yammacin Sahara, yankin da Morocco ke dauka a matsayin nata, ya dagula dangantaka tsakanin kasashen biyu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.