Isa ga babban shafi
Iran-Faransa

Macron ya damu kan yadda Iran ta fara karya ka'idojin yarjejeniyar 2015

Shugaban Faransa Emmanule Macron ya bukaci kasar Iran da ta gaggauta rage adadin sinadarin uranium da ta ke tacewa yanzu haka, bayan da hukumar yaki da yaduwar makamin nukiliya ta IAEA da ministan harkokin wajen Iran Javad Zarif suka tabbatar da cewar kasar ta zarce adadin da aka gindaya mata a karkashin yarjejeniyar nukiliyar shekarar 2015.

Shugaban Faransa Emmanuel Macron
Shugaban Faransa Emmanuel Macron Ian Langsdon/Pool via REUTERS
Talla

Shugaba Emmanuel Macron ya bayyana damuwar sa kan yadda Iran ta zarce ka’idar da aka shata mata na ta ce sinadarin uranium a karkashin yarjejeniyar ta shekarar 2015 da ta kulla da kasashen duniya, inda ya bukace ta da ta gaggauta dakatar da shirin da kuma daukar duk wani mataki da kan iya yi wa yarjejeniyar zagon kasa.

Macron ya ce zai cigaba da daukar matakin warware matsalolin da ake samu tsakanin Iran da Amurka wanda zai bai wa kasar damar cin gajiyar yarjejeniyar da aka kulla, mussaman wadanda suka shafi tattalin arzikin ta.

Ita ma kasar Rasha ta hannun Ministan harkokin wajen ta, Sergei Lavrov, ta bukaci Iran da ka da ta yi amfani da bacin rai wajen daukar matakan da ba su dace ba.

Ita ma China ta bayyana damuwa kan sabawa yarjejeniyar, inda ta zargi Amurka da haifar da matsalar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.