Mutane da dama ne suka mutu a yakin Yemen
Hukumomin Lafiya a kasar Yemen sun ce sojojin da masu tada kayar baya sama da 100 aka kashe a fafatawar da aka kwashe mako guda ana yi domin karbe iko da tashar jiragen ruwan kasar.
Wallafawa ranar:
Dakarun Yemen na kokowar ganin sun mamaye tashar jiragen ruwa da ake amfani da ita wajen kai kayan agaji ga mutane akalla miliyan 22 dake cikin halin kuncin rayuwa.
Masu aikin kula da lafiya a Kudancin Aden sun ce sun karbi gawarwakin mutane 52 da aka kashe cikin su harda sojoji 20 daga jiya zuwa yau, abinda ya kawo adadin mutanen da aka kasha zuwa 110.
Suma yan tawayen sun rasa mutane da dama a fafatawar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu