Isa ga babban shafi

Majalisan Dinkin Duniya ta damu da makomar 'yan gudun hijirar Congo

Majalisar  Dinkin Duniya ta sake gargadi cewar tabarbarewar al’amura a Jamhuriyar Dimokiradiyar Congo zai haifar da mummunar yanayi kan halin da yan gudun hijira zasu shiga.

Wasu 'yan gudun hijira a sansanin su da ke Bunia a Gabashin Jamhoriyar Demokradiyan Congo, na karban tallafin abinci da ga kungiyar likitoci na MSF,  16 ga watan Fabareru 2018.
Wasu 'yan gudun hijira a sansanin su da ke Bunia a Gabashin Jamhoriyar Demokradiyan Congo, na karban tallafin abinci da ga kungiyar likitoci na MSF, 16 ga watan Fabareru 2018. RFI
Talla

Hukumar da ke kula da Yan gudun hijira ta Majalisar ta ce Yankin Tanganyika na ci gaba da fuskantar mummunar tashin hankali, sakamakon barkewar fada da masu dauke da makamai suka kaddamar.

Mai magana da yawun hukumar, Andrei Mahecic, yace fafatawa tsakanin Yan Kabilar Bantu da Twa na ci gaba da haifar da matsaloli a kasar.

Jami’in yace sun samu rahotanni 800 da suka hada da kisa da sace mutane da kuma fyade a makwanni biyu na watan Fabarelun shekara 2018, abinda ke da matukar fargaba.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.