Isa ga babban shafi
Iran-Saudi

Iran ta tabbatar da hannun Amurka da Saudiyya a zanga-zangar kasar

Babban mai shigar da kara a Iran ya ce jami’an leken asiri na CIA ne suka taka muhimmiyar rawa wajen assasa zanga-zangar da kasar ta fuskanta a baya-bayan nan wanda kuma suka samu goyon bayan kasashen Isra’ila da Saudiyya. Tun da farko dama Iran ta zargi kasashen Amurka da Saudiyya da hannu wajen tunzura masu zanga-zangar.

A cewar Iran Saudiyya ce ta bayar da kudin da kasashen Isra'ila da Amurka suka shirya zanga-zangar don haddasa rikici.
A cewar Iran Saudiyya ce ta bayar da kudin da kasashen Isra'ila da Amurka suka shirya zanga-zangar don haddasa rikici. Tasnim News Agency/Handout via REUTERS
Talla

Kamfanin dillacin labaran Iran IRNA ya ruwaito Mohammad Jafar Montazeri na cewa kasashen na Amurka da Saudiyya da kuma Isra’ila sun kai fiye da shekaru 4 suna shirye-shiryen zanga-zangar don tayar da hankali a Iran.

A cewar Mohammad Montazeri wani bincike da hukumar sirri ta Iran ta gudanar a baya-bayan nan ya nuna cewa kasashen sun yi amfani jami’an tsaron leken asirin CIA wajen tunzura masu zanga-zangar.

A cewar Montazeri, jami’an tsaron CIA na Amurka da na Mossad da ke Isra’ila su ne suka taka muhimmiyar rawa a zanga-zangar yayinda Sa’udiyya kuma ta biya dukkanin kudaden da ake bukata.

Duk da yake gwamnatin Amurka ta musanta hannu a zanga-zangar amma Iran ta ce tana kwararan hujjoji da ke nuna kasashen uku sun taka muhimmiyar rawa wajen shiryawa dama ingiza masu zanga-zangar.

Akalla mutane 22 ne suka mutu yayinda aka kame fiye da mutane 450 yayin zanga-zangar kan matsin rayuwa a Iran wadda ta faro daga ranar 28 ga watan Disamban shekarar 2017.

Zanga-zangar dai ita ce irinta mafi muni da Iran ta taba fuskanta tun bayan ta shekarar 2009.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.