Isa ga babban shafi
Brazil

Rikicin gidan yarin Brazil ya kashe mutane 60

Akalla mutane 60 sun rasa rayukansu bayan wata tarzoma ta barke tsakanin kungiyoyin ‘yan daba a wani gidan yarin Brazil, kamar yadda hukumomin kasar suka sanar. 

Gidan yarin Brazil na fama da fadace-fadace tsakanin kungiyoyin 'yan daba
Gidan yarin Brazil na fama da fadace-fadace tsakanin kungiyoyin 'yan daba REUTERS/Douglas Jr./O Estado do Maranhao
Talla

Lamariin ya faru ne a jiya Lahadi a birnin Manaus na jihar Amazonas kamar yadda daya daga cikin masu kula da gidan yarin, Pedro Florencio ya shaida wa manema labarai.

Ko a cikin watan Oktoban da ya gabata, sai da aka samu irin wannan rikici tsakanin ‘yan daba a gidajen yarin kasar uku, abin da ya haddasa asarar rayukan jama’a da suka hada da wadanda aka kona da ransu.

Brazil na cikin kasashen duniya da ke sahun gaba wajen yawan adadin mutanen da ke garkame a gidajen yari, in da a shekarar 2014 kadai, ta kulle mutane fiye da dubu 600  a lokaci guda, kuma akasarinsu maza ne bakaken fata.

Kungiyoyin kare hakkin dan adam na duniya sun sha kiraye-kirayen daukan mataki game da halin da mazauna gidan yari ke ciki a Brazil.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.