Isa ga babban shafi
Rasha-Syria

Rasha da Syria sun dakatar da kai hari a Aleppo

Rasha da Syria sun sanar da dakatar da kai hare-hare ta sama a kan birnin Aleppo, a daidai lokacin da ake fatan fara aiki da yarjejeniyar tsagaita buda wuta, matakin da Majalisar Dinkin Duniya da Tarayyar Turai suka yi na’am da shi.

Dakarun Syria sun yi wa mutanen Aleppo kawanya a Syria
Dakarun Syria sun yi wa mutanen Aleppo kawanya a Syria REUTERS
Talla

Sai dai Amurka na shakku ga Rasha duk da ta yi na’am da matakin kasar na tsagaita wuta a yankin na Aleppo.

Majalisar Dinkin Duniya ta ce ba ta da niyyar bai wa hukumomin agajinta damar isar da kayan jin kai ga jama’ar da ke rayuwa a Aleppo duk da Rasha da Syria sun amince su dakatar da kai hare hare.

Majalisar Dinkin Duniya ta ce dole sai ta samu tabbaci daga bangarorin da ke rikici a Aleppo kafin ta tura kayan agaji zuwa yankin.

An nuna hotunan mutanen Aleppo saman titi suna tsintar abin da za su ci a yau Talata bayan an tsagaita wuta.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.