Isa ga babban shafi
Amurka

Biden ba zai tsaya takarar shugabancin Amurka ba

Mataimakin Shugaban kasar Amurka Joe Biden ya sanar cewa ba zai shiga takarar shugabancin kasar da za a yi a shekarar 2016 ba, abinda ya kawo karshen rade radin da aka dade ana yi.

Mataimakin shugaban kasar Amurka, Joe Biden
Mataimakin shugaban kasar Amurka, Joe Biden REUTERS/Gary Cameron
Talla

Wannan matakin zai bai wa Hillary Clinton damar ci gaba da jan zarenta a takarar ba tare da wani fitaccen abokin karawa ba.

Daukan matakin na zuwa ne a daidai lokacin da Biden ke juyayin mutuwar dansa mai suna Beau, wanda ya gamu da cutar Kansa a kwakwaluwarsa a watan mayu.

To amma duk da wannan sanarwar, Biden ya ce ba zai yi shiru ba a lokacin yakin nema zabe kuma zai ci gaba da tsoma baki game da makomar Jam’iyyarsa da kasarsa

A na ta bangaren, Clinton ta bayyana Biden a matsayin aboki na gari.

Biden dai ya shafe fiye da shekaru 40 yana harkar siyasa.

 

 

 

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.