Za a fara binciken jami'an fadar Vatican da ake zargi da lalata da yara
Yau Asabar ake sa ran fra bincike kan wasu jami’ar fadar Fararoma ta Vatican, da ake zargi da yin lalata da kananan yara.
Wallafawa ranar:
Yayin binciken, za a saurari batu kan wani tsohon archbishop na kasar Poland, mai suna Jozef Wesolowski, da ake zargi da mallakan hotunan Bidiyon da ake lalata da kananan yara, cikin shekarar 2013 zuwa 2014.
A shekarar 2012 aka sauke Wesolowski daga mukaminsa, bayan da aka gano cewa yana biyan yara maza kudi, don aikata lalata.
Sai dai akwai wadanda ke kallon bincike a matsayin fargar jaji, don a ganin su, an makaro a binciken dake kokarin yi kan yakin da ake yi da limaman addin kirista da ake zargi da cin zarafin kanan yara.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu