Isa ga babban shafi
MDD-MALARIA

Zazzabin cizon Sauro na cigaba da yin kisa a duniya-MDD

Majalisar Dinkin Duniya ta bayyana cewa, har yanzu akwai mutane akalla dubu 600 da ke rasa rayukan su sakamakon zazzabin cizon sauro wato Malaria, inda ta bukaci kara kaimi domin yaki da cutar.

Ana koyawa mutane yadda ake amfani da gidan sauro
Ana koyawa mutane yadda ake amfani da gidan sauro Georges Merillon/Global Fund
Talla

Majalisar ta sanar da hakan ne bayan hukumar lafiya ta duniya ta bayyana cewa, jan kafa dangane da samar da wadatattun magungunan zazzabin cizon sauran na ta’azzara matsalar magance cutar.

Wani babban Jami’i a hukiumar lafiya ta MDD, Richard Cibulskis ya shaidawa taron manema labarai a birnin Geneva da ke Switzerkland cewa, sun taka muhimmiyar rawa wajan yaki da zazzabin cizon sauran.
 

Cibulskis ya kuma ce, kamuwa da cutar a duniya ya ragu da kashi 30 cikin 100, lamarin da yasa aka samu raguwa kashi 40 cikin 100 na wadanda ke rasa rayukansu saboda cutar.

To sai dai duk da wanna nasarar, hukumar lafiyar ta duniya ta ce, har yanzu ana bukatar kara kaimi dangane da yaki da cutar

Sanarwa na zuwa ne, adai-dai lokacin da ake shirin gudanar da ranar zazzabin cizon sauro ta duniya, 25 ga watan Afrilu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.