Amurka
An bukaci Falasdinawa su biya wasu Amurkawa diyya
Wata Kotu a Amurka ta bukaci shugabannin Falasdinawa su biyya diyyar kudi Dala miliyan 218 ga wasu Amurkawa shida da aka kai wa hare hare dabam dabam a Isra’ila daga shekarar 2002 zuwa 2004. Ma su taimakawa Alkalin Kotun New York shawara ne suka bukaci a biya diyyar.
Wallafawa ranar:
Talla
Kuma sun ce sun samu Hukumar Falasdinawa da Kungiyar fafutikar ‘yancin Falasdinu da laifufuka 25 da suka hada da kashe mutane 33 tare da raunata 390.
Sai dai lauyan Falasdinawan ya ce bai dace a kama shugabanin da laifin da wasu marasa hankali suka yi ba.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu