Rahoton Amnesty yace an samu raguwar zartar da hukuncin kisa
Wani Rahotan kungiyar Amnesty International, ya nuna cewar kasashen duniya na ci gaba yin watsi da zartar da hukuncin kisa, kodayake kuma har yanzu ana samun wasu kasashen da ke aiwatar da hukuncin. Rahotan yace kasashen India, Japan, Pakistan da Gambia da suka dade basu aiwatar da hukuncin ba, sun koma aiwatar da hukuncin bara, yayin da Iraqi ta aiwatar da hukuncin kan mutane 129 bara, sabanin 68 da aka kashe a shekarar 2011.
Wallafawa ranar:
Sakatare Janar na kungiyar, Salil Shetty, yace a bara, an aiwatar da hukuncin kan mutane 682 a duniya, wanda ya zarce na shekarar 2011 da mutane biyu.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu