Mabiya Addinin Kirista suna gudanar da Bikin Kirsimeti
A Ranar Ashirin da biyar ga watan Disamba ne, mabiya Addinin Kirista a sassa daban-daban na duniya ke gudanar da bikin kirsimeti, domin murnar tunawa da ranar haihuwar Yesu da suke bautawa.
Wallafawa ranar:
Daruruwan Mutane ne daga sassan daban daban suka kai ziyara Bethlehem inda aka bayyana anan ne aka haifi Yesu.
A Bethlehem, limamin Darikar Katolika a birnin Kudus ya bayyana goyon bayansu ga samun ‘Yancin Falesdinawa.
Fafaroma Benedict shi ne ya jagoranci taron mabiya a Majami’ar St Peter yana mai kira ga Mabiya Kirista su tsarkake zukatansu tare da neman gafara ga zunuban da suka aikata a baya.
Fafaroma Benedict ya yi addu’ar samun zaman lafiya tsakanin Isra’ila da Falesdinawa tare da neman zaman lafiya a kasashen Lebanon da Syria da kuma Iraqi.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu