Isa ga babban shafi
Afghanistan

Amurka ta murkushe wani sabon hari kan filin jiragen saman Kabul

Sojojin Amurka sun kaddamar da harin sama a Kabul a inda suka nufi wani da ake zargin dan kunar bakin wake ne da ke da niyyar kai hari filin jirgin saman, kamar yadda jami’an Amurka suka sanar.

Sojojin ruwan Amurka dake Afghanistan.
Sojojin ruwan Amurka dake Afghanistan. via REUTERS - US MARINES
Talla

Jami'an, wadanda suka nemi a sakaya sunansu, sun shaida wa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa an kai harin ne kan 'yan kungiyar IS-K, dake adawa da dakarun kasashen Yamma da kuma Taliban, kuma ita ce ke da alhakin kai harin kunar bakin wake a wajen filin jirgin sama a ranar Alhamis.

Harin na IS-K, reshen kungiyar Islamic State (IS), ya kashe a kalla 'yan Afghanistan 90 da sojojin Amurka 13 yayin da ake ci gaba da aikin kwashe mutane bayan kwace Kabul a ranar 15 ga watan Agusta.

Wannan na zuwa ne bayan da Amurka ta yi gargadin cewa akwai yiwuwar sake kai wani harin ta’addanci makamancin wanda aka kai  a filin jirgin  saman Kabul.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.