Iran ta bukaci tsare mutumin da ya kai hari cibiyar Nukiliyarta
Iran ta gabatar da sunan mutumin da take so a kama shi dangane da alakarsa da fashewar da ya auku a tashar Nukiliyarta dake Natanz, wanda ya haddasa daukewar wutan lantarki kwanakin baya, yayin da tattaunawa ke gudana a Vienna a kokarin ceto yarjejeniyar nukiliyar Tehran na shekarar 2015 da manyan kasashen duniya.
Wallafawa ranar:
Gidan talabijin din kasar ya ruwaito Ma'aikatar leken asirin Iran ta bankado "Reza Karimi, amatsayin wanda ya kisa wannan aika-aika.
Sanarwar tace, wanda ake zargin ya gudu daga Iran kafin fashewar ranar Lahadin da ta gabata da kasar ta zargi Isra’ila da alhaki.
Jami'an kasashen da suka rage a yarjejeniyar nukiliyar Iran sun fara wani taro a hukumance a Vienna, suna masu cewa wannan zagayen tattaunawar da aka fara a ranar Alhamis zai kawo karshen matsalar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu