Sheikh Hasin na kan hanyar lashe zaben Bangladesh
Firaministar Bangladesh Sheikh Hasin ta lashe zaben yan majlisun kasar da ya gudana yau lahadi, a cewar sakamakon farko.Gungun masu dafawa Sheikh Hasina ne suka lashe yawan kujeru a majalisar kasar, a dai dai lokacin da jam’iyyun adawa ke bayyana cewa an tafka magudi a zaben da ya haddasa mutuwar mutane 17.
Wallafawa ranar:
Gungun masu marawa Firaministar sun lashe akalla kujeru 191 daga cikin kujeru 300 na majlisar, wanda hakan ya zarce adadin 151 dake bayar da damar samun rijaye a zauren majalisar.
Sheikh Hasin mai shekaru 71 da kuma ta share shekaru goma ta na jagorantar gwamnatin kasar ta Bangladesh na kan hanyar sake samun wa’adi na hudu a wannan kasa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu